An rantsar da sabbin shugabannin hukumar gudanarwa ta Ilimin manya a jihar Katsina.

Auwal Isah Musa | Katsina Times Ma'akatar Ilimin Firamare Da Sakandare ta jihar Katsina a ranar Juma'a 11 ga Yulin 2025,....

Katsina City News July 11, 2025  ·  12:00 AM
| 1,263 Views


Auwal Isah Musa | Katsina Times 

Ma'akatar Ilimin Firamare Da Sakandare ta jihar Katsina a ranar Juma'a 11 ga Yulin 2025, ta gudanar da taron rantsar da sabbin shugabannin gudanarwa na Hukumar Ilimin Manya Ta Jihar Katsina (State Agency For Mass Education Board Members) a babban dakin taron Ma'aikatar.

Tun farko da farko da take gabatar da jawabi a matsayin mai jagorantar bikin rantsarwar, Kwamishinar Ma'aikatar Firamare Da Sakandare Ta Jihar, bayan ta taya sabbin shugabbanin murnar kasancewarsu a wannan mataki, ta fara da jinjina ga gwamnatin Malam Dikko Radda, bisa ga yadda ta ba wa bangaren Ilimi fifiko na musamman a fadin jihar, inda ta bayyana shugabannin da ake rantsawar a matsayin tabbacin haka, domin sai da aka yi tankade da rairaya kafin a zabo su a damka masu ragamar shugancin hukumar.

"Za6o ku a shugabancin wannan hukuma na zuwa ne bayan tabbatar da Inganci, jajircewa da kuma kwazonku a tarihin aikinku."

Daga nan, Hajiya Zainab Musawa ta hore su da su yi amfani da gogewarsu tare da zage damtse a yayin shugabancinsu wajen kawo gagarumin ci gaba da sauyi mai ma'ana ga Ilimi a fadin jihar, inda ta bayyana hakan a matsayin abin da ake da fatan gani daga gare su.

Bugu da kari, ta kuma hore su da su yi aiki da kishi gami da hadin kai a tsakanninsu, don a cimma nasarar da ake bukata.

"Ba zan yi tantamar cewar za ku hada kai da aiki tukuru a tare ba, wajen taimakawa junanku da shugabarku wacce za ku yi aiki tare da ita don a cimma nasara. Allah ya yi maku jagora a yayin gudanar da ayyukanku na shugabancin wannan hukuma." Ta karkare.

Ita ko a nata jawabin a wajen, Shugabar Hukumar Ilimin Manya Ta Jihar, Hajiya Bilkisu Kaikai,Ta bayyana yadda Ilimi ke samun gagrumin ci gaba a yanzu ta kowane fanni musamman a hukumar da take wa jagoranci, sakamakon ba wa bangaren dukkan abin da yake bukata daga gwamnan jihar Malam Dikko Umar Radda, inda ta bayyana gwamnan a matsayin 'shugaba mai hangen nesa'.

Hajiya Bilki Kaikai, ta kuma bayyana Kwamishina Hajiya Zainab Musan Musawa a matsayin wadda ta yi wa Ilimin jihar allurar wartsakewa nan-da-nan, sakamakon shugabancin Ma'aikatar da gwamna Radda ya mika mata jan ragamarsa.

A bikin rantsuwar, an bayyana Dr. Aisha Ladan a matsayin sabuwar Shugabar Hukumar Ilimin Baidaya Ta Jihar, a yayin da kuma Adamu Sule (Jibiya), Nazifi Abdulkadir (Batagarawa), Hajiya Saratu Ibrahim(Danja), da Sani Maibara (Baure) a matsayin masu taimaka mata wajen gudanar da shugabancin hukumar a bangarori daban-daban.

Wadandan suka halarci bikin rantsawar sun hada da: Shugabar din-din-din ta Ma'ikatar Ilimin Firamare Da Sakandare ta jihar, Hajiya Ummul-Khairi Bawa, Babban Sakataren Hukumar Kimiyya Da Fasaha ta jihar, Farfesa Kabir Ibrahim Matazu, da kuma Shugabar Hukumar Ilimin Manya ta jihar, Hajiya Bilkisu muhammad Kaikai, da sauransu.

Advertisement

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 2 + 6?