Kungiyar Kare Hakkin Yan Adam ta Amnesty International, ta bukaci a gudanar da daya-dayan bincike a kan kisan-gayyah da wasu mutane su ka yi wa wata mata mai suna Ummulkhairi a Maraban Jos.
Wasu gungun mutane ne dai su ka kashe Ummulkhairi a ranar Lahadi, bayan sun ma ta wani zargi na karya da sunan ta na satar yara.
Ummulkhairi ta kasance Malamar Makaranta, Kuma ta baro gida ne da nufin halartar wani wa'azi tare da ya-yan ta biyu.
Ta soma kokarin tambayar mutane makarantar da a ke wa'azin, wanda daga nan ne lamarin ya kazance har ta Kai ga an kashe Kuma an kone ta.


Comments (0)
No comments yet. Be the first to share your thoughts!