An kaiwa ma’aikatan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina hari da miyagun makamai da su ka hada da bindiga, ranar Asabar da kimanin karfe 2:30 na dare. Ma’aikatan Hukumar ta Hisbah sun je hana matasa yin kwallo ne a kan titi bayan da al’ummar unguwar su ka kai koke a kan yadda matasan ke takurawa masu Sallar Tahajjud, masu Bacci a gidajen unguwar da kuma amfani da hanyar.