Tunawa Da Sojoji: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin iyalan hafsoshi da suka rasa rayukansu a....

Katsina City News January 16, 2025  ·  12:00 AM
| 1,780 Views
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin iyalan hafsoshi da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

Gwamnan ya halarci bikin tunawa da sojojin da suka rasu a ranar Laraba a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Daudaa Lawal ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 20 ga Rundunar Sojojin Nijeriya, reshen Jihar Zamfara a yayin ƙaddamar da tambarin tunawa da sojojin da suka rasu na shekarar 2025.

Advertisement

NRS Gateway

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 3 + 4?