Tsoffin Shugabannin CPC Daga Fadin Kasa Sun Bayyana Cikakken Goyon Baya Ga Jam’iyyar APC Da Shugaba Tinubu

Daga Abu Shadrach, AbujaDukkan tsoffin shugabannin jam’iyyar Congress for Progressive Change (CPC) daga jihohi 36 na Najeriya da Babban Birnin....

Katsina City News November 06, 2025  ·  12:00 AM
| 834 Views


Daga Abu Shadrach, Abuja

Dukkan tsoffin shugabannin jam’iyyar Congress for Progressive Change (CPC) daga jihohi 36 na Najeriya da Babban Birnin Tarayya (FCT) sun hadu tare da sake jaddada cikakken goyon bayansu ga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu (PBAT).

A cikin sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, tsoffin shugabannin CPC sun kada kuri’ar amincewa da shugabancin Shugaba Tinubu, inda suka yaba da irin jagorancinsa da kuma kokarinsa na ci gaba da gyara Najeriya domin samun ci gaba da kwanciyar hankali.

Taron ya kuma jaddada muhimmancin hadin kan kasa, inda aka yi kira ga ’yan Najeriya da su guji duk wani yunkuri ko tasirin waje da ke neman raba kan al’umma ko tada rikici a cikin kasa.

Manyan shugabanni irin su Sanata Tanko Al-Makura da Rt. Hon. Aminu Bello Masari sun yi jawabi a wajen taron, inda suka yabawa jajircewar tsoffin shugabannin CPC tare da yin kira ga ’yan kasa masu kishin Najeriya da su ci gaba da marawa gwamnatin nan baya wajen ganin an cimma burin gina kasa mai karfi da arziki.

Advertisement

Tags: Daga Abu...

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 7 + 3?