Wata kungiya mai rajin kare hakkin dan Adam, National Human Rights, ta kai karar wani jami'in Hizba mai suna Muhammadu Shuaibu, gaban Kwamishinan 'Yan Sanda na jihar Katsina. Wannan karar na dauke da zargin cin zarafin wasu mutane uku: Kabir Mamman, Shamsu Lawal, da Hadiza Bala.